Posts

Showing posts from November, 2019

Tsakanin Malaman Musulunci Da Masana Ilimin Kimiyya Da Fasaha: by Ustadz Abdulrahaman Muh'd Sani

Image
TSAKANIN MALAMAN MUSLUNCI DA MASANA ILIMIN KIMIYYA DA FASAHA _______________________________ _______________________________ Da yawa daga cikin wandanda suka fitinu da Turawan Yamma suke kokarin koyi da su a ko wane hali suna yawan nanata cewa addinin musulunci ko malaman muslunci suna adawa da ilimukan kimiyya da fasaha da masana wadannan ilimuka, a kokarinsu na kamanta yadda Turawan suka kasance a zamaninkan da suke kiransu da "Middle Ages" na adawa da duk wani abu da ya shafi ilimin kimiyya da fasaha da kuma yadda muslumai suka kasance ada dama yanzu. Su kan kafa hujja da yadda Malaman addinin musulunci suke daukar wasu daga cikin masana ilimin kimiyya da fasaha a tarihin musuluci wanda wannan karyace zunzurutu, manufar ita ce samawa batansu muhalli da hujja ta hanyar kiristantar da Musulunci da nuna cewa yadda Turawa basu iya samun cigaba ba sai da suka yiwa kiristanci tawaye da bore sannan suka kai inda muke gani a yau, hakanan suma muslmai sai sun yiwa addininsu taw...

Ministan Sadarwa Dr. Isa Ali Ibrahim pantami Ya bayar da umurnin dakatar da Voice mail

Image
Ministan Sadarwa na Najeriya Dr. Isa Ali Pantami  ya bai wa kamfanonin layukan waya umarnin da su daina damun masu amfani da layukan waurin tura masu sako idan an kira su ba a same su ba wato voice mail. A wata sanarwa da mai magana da yawun ministan Uwa Suleiman ta fitar ta ce ministan ya fahimci cewa abin ya fara zama ruwan dare alhalin ba a saba da shi ba a Najeriya. Kazalika mutanen da ke zaune a karkara, in ji ministan, ba sa jin harshen da kamfanonin ke amfani da shi a sakonnin sannan kuma ana cazar mutane ko ba tare da son ransu ba. "Hakkinmu ne mu kare hakkin masu amfani da layuka a Najeriya yayin da kuma muke samar da yanayin kasuwanci ga kamfanonin layukan bisa tsarin kasuwanci na duniya," in ji sanarwar. Ta kara da cewa: "Wannan dalili ne ya sa Dr. Pantami ya umarci hukumar kula da harkokin sadarwa ta NCC da ta tabbatar cewa an bai wa masu amfdani da layukan zabin samun sakonnin bisa radin kansu ta hanyar saka wasu lambobi na musamman." Copyr...

Abin alkhairi Yasa Mu Al'ummar Musulmai by Shu'aibu Muhammad

Image
*Abin alkhairi Yasa Mu al'ummar musulmai* Lallai wannan abin farin ciki ne Da nuna godiya Ga Allah Da Ya azurta wannan kungiya, da Abin alkhairi. Ya Kai ɗan'uwa kayi farin ciki Da wannan babbar cigaba data sa me al'ummar musulman (Duniya) Ba iya Nigeria kaɗai Ba, ba iya Arewacin Kasar Nan Ba. Ba kuma Wani Yanki ba. Ya Kai ɗan'uwa ka guji Yi Mata batan ci. Kamar Yadda yazo a cikin Hadisin Manzon rahama Annabi Muhammad (S.A.W) Yake cewa; "kafadi alkhairi Ko kuwa kayi shiru" Yin Hakan shine abinda Yafi Zama Maka alkhairi. Ka taimaka Da wadannan abubuwa; 1. Ka taimaka da dukiyar ka idan kana da ita, 2. Ka taimaka da ƙarfin ka idan aka bukaci hakan gare ka. Ko Kuma kayi Mata fatan alkhairi idan baza ka Iya Abinda Na ambata a sama ba. Amma ka guji habaici cikin zancen ka ko kushewa dan ba Abinda Hakan Zai anfanar da Kai. Allah Ya Taimaki shuwagabannin Mu Ya Sa su cimma ma mana wannan babbar alkhairin Tare Da Mu dasu duka, Allah Yasa a fara lafiya kum...