Kungiyar IZALA zata sakawa mutum 120 hannuwa da kafafun roba kyauta a jahar Kano

Kungiyar IZALA zata sakawa mutum 120 hannuwa da kafafun roba kyauta a jihar Kano

Daga Ibrahim Baba Suleiman

Kungiyar IZALA naci gaba da aikin samawa mutane kafafu da hannuwan roba kyauta wanda akayiwa suna da (MSIC). Shirin Wanda ke tafiya a halin yanzu a jihar kano karkashin jagorancin shugaban IZALA Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau da hadin gwuiwa da Tolaram Foundation na kasar India, tare da hadin gwuiwar Gwamnatin jihar kano.

Sheikh Lau ya kai ziyarar gani da ido a wajen aikin dake gudana a Asibitin kwararru na Muhammadu Buhari Specialist dake Giginyu Kano

Sheikh Bala Lau ya sami mara bayan shugaban kungiyar na jihar Kano Dr. Abdullahi Sale Pakistan, A wannan karon  mutane 120 suka sami moriyar  wannan aiki. Kwamishinan aikin lafia na jihar Kano shima ya sami ziyartar wajen da aikin ke gudana a madadin mai girma Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Comments

Popular posts from this blog

MEKE FARUWA A KANO: By Dr. BELLO GALADANCHI KANO

Shin Ya dace Bulama Bukarti Ya kira abinda Bauchi state Governor ya fada da wawanci? By: Muhammad Shu'aibu Gunda

WAIWAYE ADON TAFIYA (4) by USTAZ ABDURRAHAMAN MUH'D SANI RIJIYAR LEMO